*YAR. TALLA*
*CHAPTER9*
We miss 1page the printing is bad
Muje zuwa
Rabiu ya shiga mazaunin direba ya ja suka tafi. Kai tsaye Federal Medical Center suka nufa a lokacin har shabiyu na dare,ne da ‘yan mintuna.
Suna zuwa kuwa abin kada ma’aikacin wurin
cikin gaggawa aka wuce da ita Emagcncy Room da ita, Malam Bala mai allura ya tsaya sai da ya kammala masa duk wasu ‘yan shige da ficen da za ayi masa sannan yayi masa sallama ya tafi office don dama aikin dare yake. Rabi’u ya dinga zabga masa godiya kamar zai kwanta masa, abin har ya soma bashi kunya. ‘ A asibitin suka kwana washe garida safe likitan daya dubata yace yakoma ya tawo da ‘yar uwarta mace ta kula da ita, hankalin Rabi’u ya tashi yace, “Ai bata da ‘yar uwa.’ Likitan yace to gaskiya ba zaiyiwu zamanka wurin jinyaba dole saika samu mace yar uwarta koma wacece wadda zatayi jinyarta
A dole Rabi’u ya mike ya tafi zuciyarsa na faman suya, ya nufi gida a qafa a lokacin karfe takwas ‘na safe Yana isa gidan ya samu Babansu a gidan ya duqa ya gaisheshi yawaigo cikin Bacci yana kallonsa kafin ya ce
Rabi’u ka cika dan kanka yanzu gidan uwarwa ka kwana?” . ya sassauta murya kafin yace “Na kai
Saude Chemist ne daga nan mai Chemist din
yana taba ta yace wai dole sai an kai ta asibiti shine ya daukemu yakaimu asibin acan aka kwantarda ita,yanzu haka ita tana can asibitin tama samu sauqi sosai, don har tana iya gane wanda ke kanta‘. Yanxu likitanne yace inzo in taho da ‘yar uwarta mace, wadda za ta yi jinyarta.”
Kafin Malam yace wani inna laure ta hankado labule ta fito tana fadar. “Ai k0 saika nemi ‘yar iskarda zata zauna zaman jinyar badai laure ba donni hanyar asibitinma banabi ballantana in wuce ta gefensa, miyau wannan ban iya hadiya cikin asibiti, don haka ma karku sake ku sani a lissafi
Malam yaja ihsali kafin ya ce ‘Ni duk bama wannan ba Laure, shin kudin da za a biya a asibin ubanwa ya ajiye da zaibada nidai banidasu kuma ban ajiye ba, nan nace kar ka kai ta asibitin nan ammadayake kaibadan arzikibane shine saida kakaita don kanunamini iyakata. Totundakai dankankane basai kayi yadda kasoba,‘nidai kaga tafiya ta kwandala ban maganinta.’ Yana gama fada ya juya ya fice
Laure ma ta hankada labule ta shige dakinta ta bar shi nan. Rabi’u ya mike jikinsa amace ya rasa inda zai saka
Kansa haka yayita gararamba a gari daga qarshe da yaga bashi da mafita
Dole ya juya ya koma asibitin
Lokacin da rabiu ya gama koro masa bayani Mamaki ya kama, likita yace yanxu yarinya kamar Saude a kasa samun wanda zaiyi Jinyarta ‘bashi da mafita haka ya. Rubuta masu sallama aka bashi allurai da magunguna
Taji sauki sosai, dukda ba Karfi jikinta sosai. Suna dawowa gidan laure ta watsar dasu k0 kallonsu batayiba Rabi‘u ya dauki naira hamsin ya fita ya siyo mata shinkafa da wake da mai da yaji ya zauna ya bata taci sosai, .sannan ya bata magungunanta ta sha, bata jima ba bacci barawo ya sure ta, shima ya raba gefe ya kwanta
Washe gari tunda safe laure ta hau tuyar waina markadan ma da kanta ta kai shi, mamaki ya kama Rabi’u to wa take tunanin zai daukar mata tallar wainar?
Bata tankawa kowa ba har sai data gama tuyar . Wainar ta daddaura sannn ta mike ta nufi dakin da suke Saude ce kawai zaune tana shan ruwan shayi da biredin da Rabi’u ya siyo mata a waje.
Laure ta tabe baki kafin tace, “Aikin banza harara cikin duhu da kuwa a cikin babbar riga, saiki tashi ga tallar waina’ can na jiranki idan kin gama
Saude tayi saurin dagowa tana kallonta idonta ya kaWo kwalla Laure ta daka mata tsawa.
Koba zaki tallar bane kika noqe kina kwalalo min“ Wasu ‘yan iskan idanuwan ki can masu kama” ;
Dana kwarkwata, maza ki taso ke nake jira.” Ta saki labulan ta juya ta yi gaba abin ta.
Hawayen da suka taru a idanuwan Saude suka ziraro suka biyo kuncinta take shayin ya fita daga ranta ta ajiye ta mike ta fito har a lokacin babu Karfi ajikinta, donji take tamkar iska za ta dauketa.
Inna Laure ta miko mata tiren wainar tana fadar, “Gata nan ta Murtala gomace ki kawo min kudina cas bance ki Batar min da k0 sile biyar ba.’
Saude ta duqa ta dauka tana sharar kwalla, Rabi’u daya shigo ya sauke jarkar ruwan dake kansa yana kallonta jikinsa a sanyaye yace, “Ina kuma zakije keda bakida lafiya?” ,
Laure ta hayayyako masa -“To marar kunya ga kai ga fata ai ba a tambayar me aka yanka k0 idon ka bai gane maka talla ta dauka bane?”
Rabi’u ya hadiye abin da yazo masa iya wuya ‘ kafin yace “A gaskiya daukar alhakin zaiyi yawa, yarinya daga sallamota daga asibiti jiya, yau kuma a daura mata talla gaskiya da sake aiba ita kadai bace diya cikin gidan nanba, ita ma ‘Yar Baban aita isa tallar a dora mata mana k0k0 ita kadai ce diya,
amfanin nawa ake mata a cikin kudin tallar?”
“Eh lallai wuyan ka ya isa yanka, tabbas wato kai nan har girman ka ya kai ka fada mini magana. To ubanka ma yayi kadan ballantana kai, uwarku ma ba
tayi min wahalar kawarwa ba ballantana kai qaramin kwaro tallar zata tafi idan ta tafi ka hanata
Rabi’ u yace, ‘In dai cin zalin dan wani abun a zo a gani ne ai sai a yi mu gani idan abun na tsakani da Allah ne ni me yasa ba zaki dora mini tallar ba sai ita mace?”
Ta zaburo tayo kansa tana fadar, “Kai karfa kayi min rashin kunya kaji bari ganin ka ka kawo Karfi wallahi hakan ba zai hana in dake ka ba, wallahi wancan faskaren zan sa maka dan iska kawai. Bari uban naka ya zo inji idan shi ya sanya ka kai min rashin kunya idan kuma wani ke zuga ka sai inji.”
Rabi’u ya qure ta yana fadar, “Ai wallahi na gama zama wata Katuwa ta dakeni yanzu tunda na gane abun duk rashin kunya ne dan an ga babu uwarmu a gida don haka nima zagewa zanyi yanzu mutum na dukana ina Bare masa kai sai dai a kwashe shi a sume wallahi.’
Laure ta saki baki tana kallonsa cike da mamaki, yaushe yaron nan ya zama haka? Yaushe ya koyi ‘ rashin kunya irin wannan? Lallai dole ta dauki ‘ mummunan mataki a kansa.
Bayan sati daya da sallamar Saude daga asibiti da maraice ta dawo daga tallan alala, tana ajiye tiren
Inna Laure ta mika mata tsintsiya tana fadar, “Maza
ki share gidan nan ki dora sanwar tuwo da miya ki yi Wanke-wanke.”
Saude ta amsa da , ta dauki tsintsiyar ta share gidan tas sannan ta dora sanwar tuwon ta tafi tana wanke-wanke, Rabi’ u ya yo sallama ya shigo, Saude ta bi shi da kallo duk ya yi gaje-gaje yana rike da bakar leda
Saude ta yi masa sannu da zuwa ya amsa cike da kulawa, sannan ya wuce ya shiga dakinsu. Sannu a hankali Saude ta kammala ayyukanta saboda ciwon qirjin da ya addabe ta. ‘
Ta nufi dakinsu a gajiye ta kwanta tana faman numfarfashi da kyar, Rabi’u ya tsura mata idanuwa gaban shi yayi wata masifar faduwa ganin yanda alamun girma suka fara tsirowa daga jikinta, tabbas girma ya fara zuwar mata ya zame masa wajibi ya zage ya nemi kudi ya hadiye wani yawu mai daci wanda ya tsaya masa a makoshi, sannan ya janyo ledar da ya shigo da ita ya miqa mata, ta amsa, ta mike tana dubawa.
Kayan makaranta ne riga da wando da hijabi, dadi ya kama Saude cike da zumudi tace, “Yaya nawa ne?”
Kai kawai ya daga mata ta mike cikin zumudi zata sanya Rabi’u yayi saurin hanata yana fadar, ‘Kar kisa karki sakasu yanzu.”Tazumburo baki tana fadar “Kaidon Allah gwadawa fa zanyi ya
Harareta kafin yace. “Ba dai anan ba, idan gwadawa zakiyi fita tsakar gida sai ki gwada.’ Ta narke masa.
“Kai don Allah Yaya saboda me?”
Rabi’u ya zuba mata ido kafin ya ce ‘Wai ke baki san kin girma ba ne wai har yanzu ?”
Saude ta yi saurin kallon kanta kafin tace, “Nidin na girma Yaya?”
Ya ja wani dan gajeran tsaki ya koma ya kwanta ya juya mata baya.
Saude ta zauna kusa da shi tana fadar, “To yaushe za ka kai ni makarantar Yaya?”
“Gobe da safe.” Ya ba ta amsa ba tare da ya kalle ta ba. Ta yi wani ihun murna. ta kwanta gefen shi kanta saman kafadar shi tana fadar.
“Wallahi harna qagara goben ta yi Yaya, in gan ni a makaranta. To wai kuma Yaya me za a koya mini?”
Rabi’u ya juyo Yaja kunnenta yana fadar, “To sarkin tambaya, bari in kinje kya gani, barci nakeji karki matsa mini da tambaya ki Juya ki kwanta kawai
Saude tace Ai bakaci abincin ka ba.”
Jeki“ ‘ dauko idan ta gama . . kwasan nina koshi Ta dan zuba masa ido ‘To me kaci
Ya zaburo mata, “Kin ga tashi
Kije kinji, ban san yawan tambaya.’
ldonta ya ciko da hawaye, muryarta a sanyaye tace “To yanzu da yunwa za ka kwana kenan’?”
“Oh! Kaina Saude naci abinci, naci abinci naci abinci a waje haba.”
Tayi wani takaitaccen murmushi sannan ta juya ta fita. A bakin murhu ta iske nasu abincin a cikin Wata langa wadda ta gaji harta fara tsatsa taga tuwon wanda bai wuce cin mutum dayaba, shi ma badan ya qoshi ba. Haka Saude ta dauko ta koma daki ta cinye tas sannan ta fita ta maida kwanon ta dauro alwala ta dawo daki ta yi salla sannan ta kwanta
Washe gari tunda safe Saude ta yi Shara ta kai markade, ta dawo sannan ta debo ruwa cikin rijiya tayi wankanta babu soso babu sabulu, ‘ tana gamawa ta fito ta nufl dakinsu Laure na kallonta bata dai tanka mata ba, sai Ma tsakin da take ta faman ja akai akai.
Saude ta dauki kayanta ta sanya sababbi tas sun mata kyau sosai, Rabi u da ya dawo daga dibar
ruwansa ya shigo yana kallonta cike da sha’awa yace“tace yaya nayi kyau
Yace eh
mana Saude ai ke kyakkyawa ce
”Ta kada kai tana fadar, “Amma kullum mutane sai su rinka ce mini Kazama mummuna har yaran unguwar nan wai ba za suyi kawance da niba, sai dai da ‘Yar Baba, wai ita ce Kawarsu mai tsabta, ba ‘yar talla ba, amma Yaya ai ka ce ina da kyau k0?”
Tausayinta ya kara kama Rabi’u, yaji tamkar zai mata kuka ya daga mata kai alamar eh, babu alamar kuzari a jikinsa. Saude ta sanya takalmanta sannan ta mike ta dube shi.
“Taso muje Yaya, kada rana ta yi.” _
‘Rabi’u ya mike suka fita yana riqe da hannunta zuciyarsa cike da tausayawa. Laure dake zaune saman kujera ‘yar tsugunne gaban murhu tana qukkulla waina, ta ga sun fito, bata san lokacin data ture tirenba ta tashi tsaye idonta a warwaje tana fadar.
“Me nake gani ni Laure, me zan gani haka?”
Rabi’u ya kafa mata idanuwansa kafin yace “Makaranta zan kai ta baki gani ne kayan makaranta ne a jikinta.” ‘ ‘
Laure ta ce, “Karya ka ke wallahi idan kaga Saude ta yi makaranta to bana numfashi ne, don har abada ba zaku taBa morar‘ rayuwar duniya ba, in dai ina raye kuma Saude talla za tayi min ban yi niyar ta yi karatun bokon ba, wato abun ma ya zama gasa kenan, tunda an sa ‘Yar Baba kai ma bari ka kulla ka sanya ta. To baka isa ba wallahi ka yi kadan ka
nuna mini iyakata idan har banga bayan kaba to ban amsa sunana laureba wallahi.”
Rabi’u ya gifta zai wuce yana fadar, “To sai ki gayawa kaji dansu tantabaru tashi suke.”
Laure ta sa hannu ta riko Saude da qarfi tana fadar qarya kake wallahi ba zaka kai ta makarantar ba talla za ta yi min yau sai na ga qarshen danyan
kanka ba dai kai dan rashin kunya bane.
Rabi’u yace “Saketa kar ki karya ta, tunda bake kika haife taba, ba ki san ciwon taba.”
Laure tace, “Aikin banza ruwa biyun k0 ka manta nan aka kama uwarku da kwarto cikin daki?’
Ai dama shi dan zina har abada bai ganin kowa da mutunci, dan iska dan asara.”
Bakin ciki ya cika Rabi’u zuciya ta zo masa iya wuya cikin Bacin rai yace ‘Wallahi niba dan asara bane kuma uwarmu ba mazinaciya bace face kece babbar la’ananniyar da kika tura mata sharri, kuma insha Allahu a sannu sai sharrinki ya qare
Tun kafin ya rufe baki Laure ta share shi da wani gigitaccen mari mai kurmantar da qaramin yaro cikin zafin nama Rabi’u ya. dago Zai shara mata nasa marin ya ji an rike hannunsa, cikin Bacin rai Malam Bala ya shiga dauke shi da nashi marin hagu da
dama. , Rabi‘u ya dafe kunci da baki wanda tuni har ya
fashe jini ya kwararo cikin qunar zuciya Malam ke fadin
Hmm ya abin yake ne mu Tara gobe daidai wannan lokacin donjin ci gaban wannan qayataccen book din
Naku har KULLUM
*ABDULLAHI ISMAIL SALANKE*