*YAR. TALLAH*
*CHAPTER30*
Saudat’na Shiga falon taga Momy zaune hannunta rike da waya da alamar. magana ta gama tana shirin giftata. ta wuce, Momy ta riko , hannunta. saudat ta waigo da sauri tana kallonta, ‘don haka ta dawo ta raBa ta zauna zuciyarta babu “dadi. ,
~ Momy ta kira sunanta, “Saudat dan rigimar nan naki ba zai miki haqurin ki fara karatu ba, naga alamar rigimamme ne na gaske, don haka nayi tunanin a tsaida magana kawai in yaso ko a gidanki kyayi karatunki idan kina da rabo har gaba da sakandire sai ki wuce a gidanki don haka yanzu zabi yana wurin ki shin tsakanin Hamid da shi Ahmad din waye kike jin kina so a cikinsu” Saudat ta dago a sanyaye ta dubi Momy
kafin tace, “Duk ina sonsu”. Momy tayi wata tatacciyar dariya kafin tace, To idan kina sonsu duka Saudat wa kike son aura
A ciki kuma?”
Saudat tayi shiru zuciyarta naci gaba da
‘ harbawa, ta. sani sarai soyayyarta a yanzu tana
’ wurin Dr.“ Ahmad, to amma ta juya wa Hamid baya ‘
‘ anya ta yiwa soyayyar da yayi mata adalci kuwa? To shi kuma Dr din fa?
‘ ‘ “ Momy ta katse mata tunanin da cewa
. “Ki yi tunani da kyau Saudat, duka mutanen biyu duk suna qaunarki amma ni a nawa gamin
Ahmad shine wanda ya cancanta ki aura, amma kiyi tunani da zuciyarki”.
Saudat ta dago kai tana kallon Momy zuciyarta na faman harbawa tace “Momy na zabi Dr din in har kema yayi miki
Momy ta dora hannunta saman kafadarta ta dafa ta tana fadar, “Hakan shi yafi cancanta
Saudat, tashi kije Allah yayi miki albarka”.
Saudat ta amsa da, “Amin”. Sannan ta mike cikin sanyin jiki ta nufi dakinta, ta fada kan gadonta tayi rufda ciki ta dafe kanta da hannaye tamkar mai shirin kurma ihu, ta lumshe idanu tana jin zuciyarta na bugawa da qarfi tamkar zata ballo Kirjinta ta fito waje. Sai dai ta samu taimakon wata dunkulalliyar damuwa data tokare ta ta hana ta baro kirjin harta fito fili, tana so taji halin da Dr. Ahmad yake ciki, amma kuma tasan babu dama.
Tana nan kwance har aka kira sallar magriba don haka ta miqe ta nufi bandaki ta dauro alwalla ta fito ta nufi kan sallayarta ta zura dogon hija‘binta ta tayar da sallah, tana gamawa ta kishingida a saman sallayar ta Iumshe idanunta tamkar mai jin bacci, amma babu komai a zuciyarta sai dumbin damuwa. .
Tayi nisa a duniyar tunanin data lula sai ji tayi ana kwalla kiran sallar isha’I, a dole ta mike don ba
‘ da farali.
., saida ta gama sallar harta mike, zata Kara kudundunewa akan sallayar tamkar mai jin ‘ sanyi, inda rai da zuciya keta aikin rarrabe tsakanin Aya da tsakuwa anya dana dauki Dr. Ahmad ta bar Hamid ta’yi wa soyayya adalci? ‘ ‘ Ba taji shigowar Nabila ba, sai dai taji ta dafa ta tana fadar, “Aunty kizo inji Ya‘ya yana falo yana jiranki” ‘ Saudat ta yi saurin tashi zaune tare da rike hannun Nabilar tana fadar, “Wane falon Nabila?”
‘ “Falon Daddy da baki”. Ta bata amsa. » Saudat ta dan yi jim tamkar mai nazarin wani abu tamkar kuma wadda aka tsikara ta zabura ta mike ta shuri takalmanta ta fice ta nufi falon da yake tasa kai ta shiga tare da ‘yar siririyar sallamarta, ba don Allah yayi ta ita din mai ji bace sosai daba yadda za a yi ta iya jin amsa sallamar da yayi a can qasan makoshi irin ta wanda damuwa ta galabaitar da shi. ‘ Jikin Saudat yayi sanyi matuqa, ta zubawa fararen idanunsa ido, yana zaune saman kujera ya , tallabe kansa da hannaye biyu ya zuba wa kaifet
ido. Jikinta a mace ta IallaBa ta zauna. saman kujerar dake gefensa, ta kasa dauke idonta a kansa. Tsawon mintuna biyar falon tsit baka jin
motsin komai a ciki sai iskar A. C zaman shirun ya fara damunta tana son kawar da shirun, amma
kuma bata san k0ta Wacce hanya zata biba, to k0 hakuri zata ba shi? Idan ma hakurin ne ta ya ya zata ba shi? K0 Shukura za ta kira ta bashi kan wayar ta
“lallasar mata shi..
‘ Bata ankara ba sai dai ta ganshi a durkushe a gabanta, kirjinta ya yi wani mummunar bugawa saboda yadda yawa Kafafuwanta, tayi saurin ja da baya cikin kujerar, hakan ya yi daidai da riqo hannuwanta duka biyun da ya yi, tare da kiran sunanta cikin wata irin kasalalliyar murya wadda ta tilasta mata dago kanta ta kalle shi, gabanta ya yi wani mummunar faduwa, fararen idanun nan nasa tamkar an watsa barkono, gabadaya ya birice, ya canza tamkar ba shi bane wannan tsayayyen daktan jarumi mai razanar da ita ba. Ta runtse idonta da karfi saboda wani irin abu da taji yana tsurga mata zuciya.
Dr. Ahmad ya kira sunanta da wata irin dakusasshiyar murya, “Saudat ki bude idonki ki kalle ni don Allah, kar ki tsane ni wallahi ina sonki, irin son da duk duniya babu mai yi miki
kwatankwacinsa. ,
Saudat ki taBa zuciyata za kiji ki saurari zuciyata zakiji, ki kalli zuciyata za ki gane irin guguwar da ke binne a cikinta, Saudat ina sonki
son da zan iya salwantar da rayuwata a kanki, .. wallahi Saudat ina cikin fargaba tunda na bar gidan
Karkiji yaddah zuciyata KE cikin baqin ciki a dole na dauro alwala na zauna ina ta ambaton Allah
Saudat nayi sa’ a bakin .cikin ya gushe, amma damuwar da nake ciki bata barni ba har a lokacin nan na kasa runtsawa, gani nake zuciyarki na wurin‘ Hamid; da alama kuma zaki iya barina ki “ koma gare shi a kowane lokaci, wannan tunanin ne ya tilasta min dawowa Saudat don in sanarda ke cewa, idan har kika kuskuren juyawa zuciyata baya, to tabbas’ a ranar zakiji mummunan labari ~cewa na rasu, don ba zan iya rayuwa ba matukar
babu ke a tare daniba
Shirun da Saudat ta jine ya tilasta. mata bude idanunta tare da kallon inda ta ke sa ran’ yana zaune, amma da mamakinta tuni har ya kai bakin kofa, ba ta san lokacin da ta mike ba, tare da kiran sunansa.
Ya waigo da sauri tare da daga mata hannu.
Karki ce komai Saudat soyayya ta zarce duk yadda kike tunaninta, don soyayya gamon jini ‘ ce ba wai gamma gambiza ba, so haduwar zuciyane ba wai tilasta shi akeyi ba Kuma linzamin so ‘ hankaline ba wai son rai ba. Saudar kar ki tilasta wa kanki ki soni don kawai kina tunanin ya kamata ki soni, ba zan kasance mai son raiba na tilasta miki
aurena ba alhalin ba nine a zuciyarki ba. Tun ranar dana soma sonki na kasance bani da. wani buri da
Daya wuce son nagana dauwamar da farinciki a zuciyarki, na dandana miki zaqin rayuwar da baki taBa dandana ta.ba
Kuma har a yanzu haka abin yake Saudat, dolene na baki farin cikinki k0 da hakan yana nufin rugujewar tawa rayuwar dole zan baki shi, kuma nayi miki alkawarin sadaukar wa Hamid da soyayyata matukar shi ne farin cikin rayuwarki”,
Saudat taji wani abu ya tsarga mata zuciya mai kama da tsinin mashi, hawayen da suka tarar mata a idanu tun dazu suka samu damar biyo kuncinta, kuka nena gaske ya kwace mata, Wanda ta rasa dalilin yinsa.
Dr. Ahmad yayi saurin nufo ta, jikinsa na. kyarma yana Kokarin riko ta, tayi saurin ja da baya
tare da fadar “Karka taBa ni don Allah na rokeka, idan‘ har son da nayi maka bai gamsarda dodon kunnenka ba don Allah ka fadamin kalaman da zanyi amfani dasu don su gamsar da kai, ni dai in har na san abin da so yake nufi, to saboda kai ‘ne in har dai abin da nakeji a zuciyata shine so, to YallaBai na soka, so kuma kai kadai irin wanda ba zai taBa Karewa ba har abada” Shi ‘kuma hamid din fa ya zakiyi da shi Saudat? Yana sonki kamar yadda nake sonki, babu wani dalili da zaisa ki amince da daya daga
acikinmu don kawai kina ganin rashin kyautuwar ki guje masa Saudat nina fadada bakina na amince miki ki zaba wa ‘zuciyarki abin da take so, k0 da ‘ kuwa hakan yana nufin bani zaki zaBa ba, kuma hakan ba zai sa na karya alkawarin dana dauka ba, na daukaka darajarki da duk…….
“Ya isa don Allah ya isa haka!” Saudat tayi maganar muryarta a sanyaye cikin kuka taci gaba da fadar, “Don Allah ka kyale ni haka, idan nace ban so Hamid ba YallaBai karya nake, sai dai ina
so ka gane abu guda shine, irin son da nake wa Hamid ba shi nake maka ba, sonka a cikin
zuciyata ya sha bamban da irin nasa, don kuwa ka san shi murmushi yafi dariya. _
Abu guda kawai na sani shine, ba zan iya rayuwa ba inba tare da kai ba, idan har ina da rabon samun farin ciki da ‘ jin dadi a rayuwata to kai ne farin cikina, kai ne jin dadin rayuwata”.
Da sauri ya nufe ta tamkar ‘zai kamo ta, sai kace wani zautacce, muryarsa harsarkewa take Wurin fadar, “Da gaske Saudat kin amince zaki zama tawa? Zaki kasance dani yanzu da har abada? Saudat don Allah ki amince ki zama tawa ni . kadai, wallahi a yanzu kece farin cikina, ke kadai kika ragemin, kin amince min na turo da sadakinki gobe, ki fada min Saudat, ke nake
saurare”. Kai kawai ta iya daga masa ba tare da ta bar
zuciyarta tayi wani dogon tunani ba
Farin cikinsa ba zai misaltu ba a lokacin ita kanta Saudat ta tabbatar da hakan saboda yadda taga ya dawo cikin nutsuwarsa lokaci guda ya koma kan kujera ya zauna tare da sauke wata nannauyar ajiyar zuciya. Ya jingina kansa akan makarin kujerar yana sauke numfashi cikin nutsuwa, idonsa na kan Saudat wadda ta kasa zama.
Dr. Ahmad ya qakaro wani dan murmushi kafin ya ce, “Kin min tsaye akai kina kallona k0 so kike ki gano munina ne?”
Saudat tayi saurin janye idanunta a kunyace tare da‘ yar dariyarta Kasa~qasa.
Dr. Ahmad ya dan. kishingida kadan a kan kujerar yana fadar, “jeki samo min dan wani abu inci kada yunwa tasan yadda tayi dani
A, dan sanyaye Saudat ta kalle shi, shima ‘idanunsa a kanta suke adole ta juya ta nufi kofa don kwarjininsa ba zai barta ta furta abin da ke bakinta ba. Kai tsaye kicin ta nufa ta soma dawainiyar sama masa abin data san zai iya ci, sai dai babu komai akicin din sai sauran farfesun dare wanda yaji kayan yaji, don haka ta zubaruwa a kettle ta kawo garin citta da karunfari da ganyen
ta zuba, sannan ta jona a wuta ‘ Tana nan tsaye harya tafasa sannan ta juye masa“ta dora saman tire ta dora kofi daya tare da cokalin shan tea, sannan ta dora kular farfesun tasa filet da madaidaicin spoon sannan ta bude tirij ta dauko cake manya guda biyu ta dora a gefe, sannan ta dauka ta shiga falon da yake da sallamarta har a lokacin yana nan a kishingidensa; . Saudat ta durkusa a gabansa ta zuba masa tare da tsiyaya’masa ruwan zafi a kofi tasa masa lipton da coffe tare da madara da sukari kadan ta juya ta miqa masa yasa hannu ya karBa, bakinsa dauke da murmushi yace “Na gode kwarai”
Murmushi kawai tayi ta mike ta koma kujerarda ke fuskantarsa ta zauna.
Tana kallonsa sai daya cinye komai ita kanta tayi mamakin irin yunwar daya kwaso, shi .kansa ya lura da irin kallon da take masa. Ya mike tsaye da dan murmushinsa yana kallon agogon dake daure a hannunsa, yace “Ni zan wuce, idan har kallona da kike me cike da tuhuma ya wadatar dake!!! Murmushi kawai tayi, ta mike tana tattara, kayan daya ci abincin, ya dan mirgina kai ‘
”‘idan kin shiga gida ki sanar da Momy
manya zasuzo gobe insha Allahu misalin qarfe hudu na yamma”
Allah ya kai mu’ ta amsa a takaice tare da bin gefensa zata wuce saboda kwarjininsa da takejin ya cika mata falon. Shi kansa ya lura da hakan, cikin zolaya yace. “Ba sallama kuma Madam ko har na angwance tun yanzu ne?” Bata juyo ba tayi gaba abinta saboda dariyar da taji yana mata, ta tabbatar zolayarta yake sonyi, don haka ta yi cikin gida abinta. Washegari misalin karfe sha daya na ‘safe; Saudat na kwance a falonta saman kafet tayi matashi da filon kujera tana kallon wa’azin Shekh
Ja’afar da aka sanyo na Sunna T.V mai taken‘
‘Suffatus salatun nabiyi’. ‘
A Kasan zuciyarta kuma tunani ne barkatai, tun jiya data yi mafarkin Yaya Rabi‘u’ ta kasa nutsuwa, tunanin dan uwan nata ya addabi ‘ zuciyarta k0 karyawa ta kasa yi, burinta bai wuce nata koma Dandagoro bA don ta karbi saqon da Hamid ya sanar da ita Yaya Rabi’ u ya bada makotansu a ajiye mata,ba ta san gidan ba zai wuce gidan Inna mai danwake ba, don gidanta ne ke manne da nasu, kuma nan ne kadai gidan da suké ‘ shiga ita da Yaya Rabi u alokacin suna tare
Bataji shigoWar Momy a falon ba, sai dai‘ taji ta dafa ta tana fadar, “Bacci ne k0 kuma dogon tunani?’
“” Saudat ta yunkum ta tashi zaune tana kallon , mahaifiyar tata wadda ke kokarin zama a kan kujera, taja remote ta rage sautin akwatin talabijin din tana fadar.
‘ “Yanzu Alhaji ke sanar dani yau za suje wurin Babanki don nema wa Ahmad aurenki, ni dai cewa ma, nayi,,kawai a kyale shi aCi gaba da
,hidima a nan, Alhaji yace ba zai yiwu ba, dole a ba
shi hakkinsa a matsayinsa na mahaifi.
Ya kike ganin za a bullo wa tsarin bikin, don rana kawai za akira ban da asabar din gobe ta sama za a daura auren, kin ga dole musan abin da za a shirya don kar lokaci ya qure mana. Ki min lissafin duk abin duk abinda kike so, don zan tura a Dubai . za a hado komai” ,. .
‘ Saudat ta sunkuyar da kanta tana wasa da
yatsu. Momy ta kafa mata idanu muryarta a saayaye tace, “Saudat lafiyarki kuwa, meke damunki?”
‘ A hankali ta dago kanta ta kalli mahaifiyar ‘ Kata da idanunta, wadanda suka ciko da kwalla, ta ,
hadiye dunkulalliyar damuwar data ‘tokare mata .
zuciya, kafin tace “Momy yanzu shi kenan Yaya
Rabiu ya bace kenan har abada?”
DAGA
*ABDULLAHI ISMAIL SALANKE*