Yar tallah31

                *YAR.   TALLAH*

                *CHAPTER31*

Momy taja wani gWauron numfashi kafin tace “Inji waya fada miki Saudat? Ni inaji a jikina Rabi,u yana raya, kuma yanzu haka na_ baza ‘ cigiyar‘sa tun daga gidajen talabijin, radiyo, mujallu  da kuma jaridu tare da ofisoshin jami,an : tsaro insha Allahu Saudat zai bayyan, ki kwantarda hankalinki kinji Saudat ta daga mata kai kafin tace, “Tun  ina Abuja Hamid ya sanar dani Yaya Rabi’u ya bada sako a makwabta a bani nasan gidan Inna mai danwake ne shine nakeson  inje inkarbo Momy tace, “A‘a ba zan iya barinki kije ba, sai dai inwa Alhaji magana yasa k0 direba ne yaje ya karbo miki hakan yayi miki?” ‘ Kai kawai Saudat ta iya daga mata alamar eh. ’ . ‘ Tace “Okay lissafo min abubuwan da kike bukata, kodai kin bani wuqa da nama ne? . Saudat ta amsa da, “Eh Momy”. Dariya Momy tayi kafin tace ‘Wannan fillancin naki yayi” yawa Saudat, anya kuwa?” ‘ ‘ Dariya kawai Saudatvdin tayi  mahaifiyar tata ta fita ta barta , Misalin karfe budu na yamma Shukura taxo , “ gidan da‘ yar qaramar jakar kayanta, dadi ya cika’ Saudat don kwana biyun da tayi babu ita ba’ ” ‘qaramin kewarta tayiba
Shukura ta sauke jakarta a kan gado tana
fadar “Amarya kin sha kamshi, wannan fara arfa duk ta murnar amarcin ne?” Saudat ta waro ido cikin dariya tace“Kai _
don Allah meye na zolaya kuma? ’ ‘
‘ Shukura ta fadakan gadon tare da rungume ta tana fadar, “Ba wani  zolaya, gaskiya na fada” ‘ Saudat ta tabe baki ta zauna a kan kujera tana fadar, “Ai dama Hausawa sunce idan baka
iya sharri ba ka koyi kage” .,
Shukura tace, “Ba wani nan, haka nan kike nuna wa Momy kauyanci amma irinku sululu kasau kunfi kowa iya shege
Saudat tasa dariya tana fadar, “Yau kuma da mita ki kaxo  gidan kenan?”
Shukura tace “Ai dole in miki iya shege, don Momy ce ta kirani wai na tattaro na taho mu zauna don ta lura kina bukatar huduba ta, ni kuwa
Tasan ba wani nan k0 karya na fada?”
Saudat ta mike tayi hanyar‘fita daga falon tana fadar, “Ni ban iya abin da kika iyaba
Shukura ta tuntsure da dariya don ta san ta
Qular da ita.
, Washegari da safe suna zaune a falo Shukura na karanta wa Saudat wani littafin Hausa mai suna KADANGARUN BARIKI, Momy ta turo
Kofar ta shigo tare da fadar, “To sai ku tashi ku shirya yanzu maza direba ya kai ku gidan Maman ‘ Sumayya maida tsohuwa yarinya” . ‘ ‘ Shukura ta zabura tana fadar, “Wow Momy! Da gaske?” . ‘ Momy ta yi murmushi tare da Juyawa tana fadar, “A’a da wasa”. , ~ Shukura ta dafa Saudat tana fadar, “Kai . amma wallahi Momy tanaji dake Saudat, lallai zaki rudar da DR wai baki taba jin labarin Maman Sumayya a Abuja ba?” Saudat ta girgiza mata kai a hankali, don ita ‘ dai bata fahinci inda maganar tasu  ta dosa ba. , Shukura tace, “Lallai, da mamaki don a  fadin Nigeria babu jihar da sunan matar nan bai , zaga ba, kaya take siyarwa ‘yan gaske, tun daga kan, gyaran gashi, gyaran fata, sabulluka zuwa mayukan gyaran fata, kayan manyan mata kuwa wannan daga qasashen Larabawa take hada su. Ke dai bari ‘ muje zaki gane wa idonki”  Saudat ta ce, “Ita kuma amarya har wani . gyara na daban ake mata.” , Shukura tayi wani takaitaccen murmushi kafin tace “In ban da abinki Saudat, idan akwai . macen da take bukatar gyara ai a bayan amarya take  ko kuma macen da ta haihu ita amarya ana bukatar ‘ komai nata ya xama na musamman ne tun ba ke da”
Zakiyi aure gidan kishiyaba, ya kamata ta ko’ina , mijinki’ ya san da bambanci, tun daga tafukan , hannunki, labbanki, fatar“ jikinki, da kuma fuskarki, sai kuma can ainahin wanda wannan kuma aikin manyan mata ne musamman idan auren na Soyayya ne
Abin da dai nake so ki gane shi ne ranar bikin kowace mace to awurinta wannan babban ra’na ce da babu irinta a rayuwarta, musamman idan auren na soyayya ne.
A ranar daurin aurenki kowa burinsa ya ga irin kwalliyar da zaki yi, kek0 da ‘yan gidanku ne suna son qare miki kallo a wannan ranar, shi yasa wasu matan tsabagen son gyaran jiki har gyaran ‘sai yazo ya yi yawa, ya feSo musu ‘da quraje a fuska k0da kuwa ada bata da wadannan kurajen Don
haka a matsayinki na aMarya ya kamata ki kula da kanki, akwai sirrikan abubuwan dake gyara amare na farko a matsayinki na amarya ana bukatarki da yawan sham ruwa sirrin hakan shine, kar jikinki ya yankwane. Sannan ana bukatar amarya da cin “ya yan itatuwa hakan zai taimaka wa fatar jikinta matuka, ‘ sannan ana bukata: amarya da ta yawaita sham , kankana, itama za ta taimaka mata matuka wurin gyaran fatar jikinta, haka kuma cin ganye irin su.  latas da kabeji,  suma za su taimaka kwarai.
Ta yinkura ta nufi bandaki tana  fadar “Bari in  fara watso ruwa mu shirya tun
kafin Momy ta sake biyo mu” . Ta zame kayan jikinta ta shige bandakin don
watsa wa jikinta ruwa. Iko sai mai tsaga ido Allah Almusawwiru, mai yadda Yaso, tabbas na yarda komai nufi ne na Ubangiji, kuma al’amarin aure tamkar layin markadene idan layi yazo kanka k0 bakaso sai an maka, kamar yadda arziki bai isa ya guje wa ‘mai shiba, haka shi ma rai bai isa yaqi mai shi ba, haka matar mutum ba ta isa ta guje‘masa ba k0 ana ’ ha-maza ha-mata, auren da Ubangiji ya qaddara   tofa sai an daura shi duk tsananin wuya, kuma duk dadi don duk nisan dare gari zai waye. Hakan ce kuma ta kasance don yau ita ta kasance ranar juma’ar da za a daura auren Saudat gidan Dr. Mariya acike yake da yan uwa da abokan arziki na kusa da na nesa, don ‘ a ranar ne za a yi kamu, wanda Dr. Mariya ta shirya . Biki ne ake ba wai na wasa ba, don kudi ta ke kashewa tamkar tana tsinto su mafiyawancin abubuwan da ake yin amfani dasu a wurin bikin duk
daga qasashen waje ta bada saqonsu aka taho mata‘ ‘ dasu
Duk Wanda ya ”san Saudat kuwa yanzu” idan ya ganta da wuya idan zai iya ganeta Cikin sati ~daya tayi wani fitinannan haske, don har wani
.yalo-‘yalo take, fatar jikinta ta yi wani luwai-luwai
’sai sheki ta ke tare da daukar ido tamkar jikin tarwada, cikin lokaci guda ta rikide tamkar wadda aka Kara wa kyau da fari.
Kodayake irin manyan kudin da Dr. Mariya
ta saki wurin gyara ‘yar tata sun isa ace  ta mafi haka. don k0 gyaran jiki sau uku aka mata arana, safe da yamma da kuma lokacin kwanciya bacci, don daidai da Kunshi daga Abuja ta dauko mai zanen da tayi musu, gyaran gashi ne aka yi musu ’ a babban wurin gyaran gashin dake G. R A,abinka dama da mai abin don haka gashin ya isa saukowa , har tsakiyar bayanta, ga wani baKi da sheqi da yake na musamman. Haka dinkunan fitar .biki duk a Lagos ta bada aka dinko mata wasu kuma a -. Dubai sai shaddojin ne ta bada aka dinkosu a Maradi. Yanzu haka Saudat ce da Shukura baje a falo suna duba kayan fitar kamun da zasu sanya a  yau, Momy ta turo kofa ta shigo da sallamarta, ta ‘ tsaya daga bakin kofa jikinta a sanyaye tace “Direba Ya daWO yanzu‘ amma har yau dai mai . danwake bata dawo ba, sai dai maigidanta ya
’tabbatarda cewa, duk abin da aké ciki ba zata wuce rana  ita yau ba tare da ta dawo ba” ‘
Cikin nutsuwa Saudat ke kallon mahaifiyar tata, cikin sanyin jiki da sanyin murya ta amsa da, “Allah ya kai mu Momy, Allah Ubangiji ya
bayyana mana shi ma kafin lokacin” .
, Momy ta amsa da,“Amin”. Kafin ta dau  wani nannauyan numfashi tana kallon Shukura tace “Ya kamata fa kuyi azamar shiryawadon Karfe hudu daidai za a fara kamun”.
Shukura ta amsa, “Insha Allahu Momy
yanzu za mu shirya”. ‘ ‘ Momy ta juya ta fice Shukura kuma ta mike tana fadar, “Tashi‘ yar uwa ki fara shafawa jikinki ruwan lallen nan kafin in fito daga wanka”
K0 motsi Saudat ba tayi ba ballantana ta sa ran amsawarta, hakan ya sa Shukura waigowa ta dubi inda Saudat ta ke, tare da fadar,“Lafiya dai Saudat. ” ”
A hankali ta dago kanta tana kallon Shukura kafin ta ce, “Babu komai”.
” Shukura ta girgiza kai, “A’a ban yarda ba Saudat, na lura damuwar dan uwanki na damunki
amma ya kamata ki yi wa Momy uzuri, saboda yadda ta ke iya bakin qokarinta bai kamata ki Kara , daga mata hankali da damuwarki ba. Kina kallo tun ‘. ranar daki kace mata yayanki ya‘ bada sako
gidan mai danwake a ajiye miki Momy kullum sai ta tayar da direba yaje gidan, amma har yau ba a yi nasarar sa’mun mai danwaken ba, tunda an ce ta je
garinsu Ki kara haquri don Allah Saudat, insha Allah zaki ga sako mai dadi wurin mai danwake da
zarar ta dawo tashi ki rage kayan jikinki in taya ki shafa
‘ Ba musu Saudat_ ta yun kura ta mike don ta sani haquri ya zame mata dole, k0 da ba a ba ta ba ita. ta bawa kanta tunda dai babu wanda ya san inda Rabi’un yake. Shi kansa Dr. Ahmad din yanzu iya kokarinsa yake mata a kan“ cigiyar dan uwan nata’ saboda yadda ya ga ta damu a kansa. , ’ Da taimakon Shukura da kuma na matar da ‘ . Momy ta dauko mai kwalliyar amare, aka gyara amarya Saudat cikin wani tsadadden cotton lace  mai laushin gaske kalar dark pink an qawata shi da bakaken fulawoyi da wasu qananun duwarwatsu, masu kama da yarfin gwal, daurin kallabin da aka kafa mata duk wanda ya kalla ya san daurin‘shago ne don ba irin wanda muka sabayi bane gashin ’ nan nata an saki kadan gefen fuskarta sauran kuma an nade shi an saki jelarsa a kan gadon bayanta inda
aka kawata wuyanta da kunnenta zuwa yatsun
hannunta da tsadaddun gwala-gwalai Sannan suka dora ta a kan bakin takalmi mai matsanancin tsini sai kace wadda ta hau tsani
sai yar qaramar jakarsu wadda bata wuce girman tafin hannuba
Amarya kam ta fita batun bayyana irin
kyawun da tayi ma bata lokaci ne, don k0 lokacin .da ta ke zama a kan kujerar da aka tanada
‘ don amarya, saf ta zauna tamkar mutum-mutumi, ko ace aljana don kyau, kai ka zata zana ta aka yi ba ‘ wai mutum bace
“Ana kiran sallar magriba aka tashi daga kamun, a lokacin ne kuma Dr. Ahmad da abokansa ‘ ‘ suka iso gidan cikin tsadaddun motocinsu, don
haka gidan ya kara rikicewa, Shukura ta shiga busy
don ganin ta karrama angwayen da abubuwan ciye ciye da tande-tande.
Saudat kuwa duk kunya da nauyin Dr Ahmad ne ya hana ta sakewa da kyar Shukura ta samu taje ta gaishe shi  shima sai da ta yi da gaske a lokacin da ta shiga falon da aka sauke su gogan nata yana kishingide saman doguwar kujera abokansa sun sa shi a gaba suna ta hayaniyarsu, ‘ inda shi kuma yake ta faman kallonsu yana cin , tuffa apple.
Saudat ta ji tamkar ta nutse a lokacin da  suka hada idanu, sai taga ma tamkar shima kara masa kyau akayi, farin yadin neke jikinsa ya  Kawatar  Da kyar ta yi ta-maza suka gaisa da  abokan nasa sarakan surutu kamar zasu hadiyeta
Kowa burinsa ya fadi albarkacin ” bakinsa ita dai ta gaza tofawa sabuda kwarjinin da angon nata ya cika falon,dashi ji take duk girman  dakin yayi mata kadan, sauqinta ma daya Shukura data tare ma rigimar domin don kuwa ita
wurin dan banzan surutu ba ‘daga baya ba. Dr. Ahmad wanda tunda ta shigo falon bai * ,tanka ba har sai da ya lura zolayar abokan nasa za ta iya nutsar da Saudat cikin qasa don kunya, ~ sannan ya yunqura ya mike a kasale tamkar wanda aka yi wa dukan tsiya.
, Ya nufi inda amaryar tasa ta ke nutse cikin kujera ya sa hannu ya tayar da ita tsaye yana fadar, “taso mu bar nan Madam kada su samin ke ciwon kai
Kamar jira suke suka yi kansa, amma bai kula suba yana rike da hannunta suka fice daga falon
kai , tsaye harabar waje suka nufa, ya jawo musu wasu fararen kujerun roba suka zauna cikin rumfar da aka tanada don hutawa
Dr Ahmad ya yi wani murmushi mai kama
‘ ‘da dariya lokacin da yake Kokarin lallai sai ya hada , ido da ita amma ta Ki yarda shi dariya ma ta ba  shi, ya tallabe kuncinsa yana fadar, “Oh ni Ahmad na ga ta kaina, haka zamu yi dake kenan?”
Ya Kara sa dariya, “Lallai yarinya aiki ya , ganki bama kadan ba, amma fa kin yi kyau don‘ lokacin da ki ka shigo falon sai da nayi suman wucin gadi har wani kishi na ji ya yunkuro min yadda na ga kartan nan na kallonki shi ya sa na harna .gaza magana
, Duk yadda zuciyar Saudat ta ke cike da alkunyarsa sai da dariya ta kwace mata jin yadda ya kira wayayyun abokansa da qartai, Dr. Ahmad ya kafe ta da manyan idanunsa yadda ta ke dariyar ’ tata cikih nutsuwa
kallon da yake mata ya sa a dole ta gimtse dariyarta, hakan ya yi daidai da sauke wani gwauron numfashin da ya yi tare da lumshe manyan fararen idanunsa ya shafi sumar qeyarsa yana kallon farar moter da take shigowa cikin gate din ’gidan a dan nesa da su kadan aka faka motar daga ita har shi idonsu na kan motar.
Zuciyar Saudat ta yi wata mummunar bugawa lokacin da mutumin da ke cikin motar ya fito shi da wata zukekiyar mace kai tsaye inda suke zaune suka nufo har a lokacin kirjin Saudat bugawa yake ta gaza k0 da kwakkwaran motsi.
“Hamid dinne k0? ’
, Dr. Ahmad ya watso mata tambayar yana . kallonta Kai kawai ta iya daga masa don a lokacin har sun qaraso cikin sallamarsu inda Hamid ya
miqawa Dr Ahmad barin fuskarsa ‘dauje da fara a suka yi musabaha Hamid na riqe da hannun ‘ Dr Ahmad ya taya shi murna tare dayi masa fatan aikhairi cikin sanyin jiki, Saudat ta gaishe shi amma ga mamakinta har a lokacin da fara,a  akan fuskarsa ya amsa mata a. tare dayi mata fatan aikhairi ya nuna zukekiyar macen dake tsaye ” wadda akalla shekarunta ba zasu haura ashirin da daya ba . Yacé, “Ga Kausar nan takanas ‘muka taho‘ tare don ta taya ni murnar aurenki, ita ce amaryar ‘ tawa“. Ya juya kan Kausar din, “Kausar ga Saudat ’ Da‘ fara’a a fuskarta ta miqa wa Saudat hannu suka’ yi musabiha cikin sigar zolaya ta dubi Dr. Ahmad tana fadar, “Godiya mara: adadi, .ka taimake ni tunda ka kasa‘ angona don da yanzu Kausar ta shiga cikin jerin sahun matan da za ayiwa kishiya a wannan watan,na gode ‘ Dariya suka yi su dukkansu ganin yadda Dr. ‘”‘ Ahmad ya Saki fuska babu alamar damuwa a yanayinsa ya sa Saudat ta saki jiki ta mike ta riko hannun Kausar tana fadar, “Bismillah‘ yar uwa mu
shiga daga ciki mu gaisa sosai ” Dr Ahmad ya mike shi ma tare da miqa wa Hamid hannu yana fadae “Ni ma abokina. mu shiga
daga ciki gida na kula abin yar wariyar launin jinsi ce”. , Duka dariya suka sa suka rankaya suka nufi
cikin gidan
Zuciyar Saudat fes, ba qaramin dadi tajiba
Ganin yadda Dr. Ahmad ya karBi Hamid din cike da ‘ farin ciki. Ba Karamin mamaki‘ ta yi ba yadda Hamid ya samu labarin aurenta, kodayake auren da kullum sanarwa ake a gidajen tal’abijin da radiyo lallai ita kanta ta san ba Karamin matsayi Hamid yake da shi a Zuciyarta ba, har cikin  ranta ta ji Kausar ta kwanta mata don kawai tana matar Hamid hatta rasa inda’zata_saka ta, ta kawo mata wannan ta’ kawo wancan har sai da Kausar ta dakatar da ita, ita kuma Shukura ta ci gaba da dawainiya da Hamid din. ‘ . Ba su suka bar gidan ba sai qarfe goma na
dare don sai da suka gaisa da Momy da Alhaji . Ashiru sannan suka tafi a cewar gobe Hamid zai maido , Kausar  gaskiya su duka sun yaba da ‘ matar Hamid din don ba qaramar kyakkyawar mace ya samu ba, wayayyiya kuma yar boko. ’ Ba Saudat ba hatta Momy da Shukura sunyi _ mamakin irin makudan‘ kudin da Hamid din ya baiwa Saudat wai ta. siyi abin da take So, tunda ‘bai _ samuya siya mata komai ba. Lallai Hamid ya
dauki Saudat da muhimmanci a rayuwarsa, haka dama al’amarin Ubangiji yake
.Washegari ita ta kama ranar asabar da misalin qarfe daya na  rana aka daura auren ” Saudat da angonta
Dr Ahmad Mukhtar ; daurin aure ne   wanda ya tara manyan mutane kala daban-daban tun daga gida Najeriya har zuwa sauran Kasashen qetara  tabbas daurin auren ya kafa tarihi a cikin Dandagoro ‘
Motoci suka dauki amarya da tawagarta zuwa gidan mahaifinta da ke Dandagoro don wai a can ne za,a dauki amarya, kamar yadda Alhaji Ashiru ya bukata ba don ran Momy yasoba ta amince
Haka manyan motoci suka kwashi amare aka nufi gidan mahaifinta, amarya’ Saudat dake lullube ‘cikin mayafi Kirjinta ya shiga dukan tara-tara don ba tasan irin tarbar da dandazon Jama,ar zasu  samu a gidan nasu ba. Haka suka shiga cikin
gidan mahaifiyar Shukura da 
DR murja qawar Momy na riqe da amarya har cikin gidan. Inna Laure dake durkushe bakin murhu na ganinsu  ta zabura ta mike tsaye tamkar sabon kamun hauka ‘ : Fuskar nan tata dukta  gauraye da majina  da ‘ hawaye saboda hayakin wuta ciki kaduwa take fadar, “Wannan dandazon haka fa sai kace na masu zuwa  yaqi na menene?
‘ Dr Murja tace“Au maigidan naki bai
Fada miki bane? To amarya ce aka kawo gidan ubanta a dauke ta a ciki”.
‘ Kida a ruwa mai tada haukan dodo tana
fadar haka Inna Laure tayo kanta da masifa, ‘
‘Amaryar uban abun uba za a kawo gidan ubanta,
k0 ita uwar amaryar bata sanar muku ba ‘yar tata ruwa biyu bace? Ai bata da uba don haka an dai daura aure a gidan nan amma babu dan iskan daya isa ya-shigo min gida don aci min zarafi
Mahaifiyar Shukura ta kwantar da murya tace, “Haba baiwar Allah meye kuma abin cin fuska don’ dai kawai dan zaman da za a yi wanda bai =wuce na minti talatin ba?”
Ai kamar jira take ta koma kanta, “Ke rufe mani baki kinji tsohuwar banza, ai dama garin ‘banza a farau-farau din wofi yake qarewa, gida dai nawa ne, kuma dole ku bar min abuna in ba haka “ba’wallahi sai in cinna wa gidan wuta mu hadu mu duka mu qone zaku fita k0 kuwa ba zaku fita ba?” Ai kafin wani ya bata amsa ta kwaso itacen dake cikin wutan tayo kansu  Malam Bala dake kokarin shigowa cikin gidan yayi wani kukan kura gamida yin kanta ya riketa ta ‘baya, hakan ya sata fasa wani razanannen ihu tana kokawar kwacewa, ya murde hannunta ya na cewa

Mu tara gobe
*ABDULLAHI ISMAIL SALANKE*

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *